Tambaya ta 30. Me cece addu'ar shiga kasuwa?

Amsa: "Babu abin bautawa da cancanta sai Allah Shi kaɗai yake ba shi da abokin tarayya, mulki nasa ne, kuma godiya tasa ce, Yana rayawa kuma Yana kashewa, Shi ne rayayye wanda ba ya mutuwa, dukkanin alhairai suna hannun Sa, kuma Shi Mai iko ne akan dukkan komai". Al-Tirmizi da Ibnu Majah ne suka ruwaito shi.